
Gwamnatin jihar Kano ta sanar da haramta gudanar da sallar Juma’a a kan manyan titunan jihar. Sheikh Al-Kasim Abbas, mataimakin kwamishinan shari’a na jihar, ne ya sanar da wannan sabuwar doka.
Toshe hanyoyi yana haddasa jinkiri ga jama’a, musamman masu zuwa asibiti ko wasu ayyukan gaggawa.
Kare rayuka da lafiyar masu salla da sauran masu amfani da hanya.
Gwamnati ta gargadi dukkan masallatan Juma’a da su tabbatar jama’arsu ba su fito kan titi ba, inda ta jaddada cewa duk masallacin da ya saba wannan doka zai fuskanci hukunci.